Burin mata a Najeriya na samun kaso talatin da biyar na guraban siyasa ya gamu da cikas bayan da majalisar dokokin kasar ta yi fatali da kudurin a farkon wannan watan, lamarin ya harzuka mata suka gudanar da zanga zangar lumana a birane da dama na kasar, da kuma lasar takobin ci gaba da tada kayar baya sai hakar su ta cimma ruwa.
Batun da shirin Domin Iyali ya fara haska fitila ke nan a wannan shirin. Bakin da muka gayyata sun hada, tsohuwar Ministar mata Aisha Isma’il, da Barrista Hassana Ayuba Mairiga, da kuma ‘yar gwaggwarmaya Balaraba Abdullahi:
Saurari tattaunawar da Madina Dauda ta jagoranta.
-
Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.