Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Farkon Dimokaradiyya A Jamhuriyar Nijar


Ginin majalisar dokokin kasa a Yamai, babban birnin Nijar
Ginin majalisar dokokin kasa a Yamai, babban birnin Nijar

Babban taron muhawara na kasa da ake kira conférence nationale, na ranar 29 ga watan Yuli na shekara ta 1991, shine ya bada damar girkuwar tafarkin dimokaradiyya a jamhuriyar Nijar, wanda hakan ya bada damar bayyanar jam’iyyun siyasa daban daban.

A shekaru 25 da gudanar da wannan babban taron muhawara na kasa, jamhuriyar Nijar ta samu shirya zabuka daban daban har guda 5, wannan zaben da za a gudanar yau 21 ga watan Fabarairu ya kasance na 6 da jamhuriyar Nijar ta shirya a tarihin zabe.

Koya ake kallon tafarkin dimokaradiya a shekaru 25 din da suka gabata? Tambayar kenan da wakilin Muryar Amurka a Nijar Yusuf Abdoulaye, ya yi wa Alhaji Issoufou Bashar tsohon jami’in difilomasiya a Nijar.

Alhaji Issoufou, yace yanzu siyasa ta kara lalacewa a jamhuriyar Nijar, domin yanzu ba a amfani da ra’ayi sai dai a saya da kudi, wanda hakan shike ci wa mutane tuwo a kwarya.

Wannan zaben na da matukar muhimmamcin gaske domin ya kasance zabe na biyu da wani farar hula ya shirya bayan ya kammala wa’adinsa na farko. Wani abu kuma da ake ganin yana da muhimmamci a zaben shine samun yan takara da yawa a bangaren matasa, kama tun daga takarar yan majalisar Dokoki zuwa na shugaban Kasa.

Yan takarar neman shugabancin Kasa 15 ke fafatawa a zaben na yau, san nan 5200 a bangaren yan majalisar Dokoki.

please wait

No media source currently available

0:00 0:04:44 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG