Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Fatan 'Yan Majalisar Dokokin Najeriya Ga Majalisa Ta Tara


'Yan Majalisar Dokokin Najeriya
'Yan Majalisar Dokokin Najeriya

Majalisar Dokokin Najeriya da ke dauke da wakilai da kuma na dattawa 469 ta dauki rantsuwar fara aiki da sababbin shugabaninta Ahmed Lawan Shugaban Majalisar Dattawa da Femi Gbajabiamila Kakakin Majalisar Wakilai, inda suka yi alkawarin yi wa kasa aiki domin ta ci gaba.

Sanata Barau Jibrin daga Jihar Kano ya ce za su hada kai da bangaren domin adawa da dukkan bangarorin gwamnati domin kasa ta ci gaba.

'Yar Majalisar wakilai Khadija Bukar Ibrahim ta ce tana fatan ganin Majalisa mai hadin kai tare da yin ayyukan da mazabunsu ke so a matsayinsu na wakilan jama'a.

Da ya ke yau rana ce ta dimokradiyya, tsohon dan majalisar wakilai mai wakiltar Birnin Gwari da Giwa a Jihar Kaduna Hon. Hassan Adamu Shekarau, ya yi kira ne ga mahukunta da su gaggauta daukan mataki akan harkar tsaro da ke damun kasar saboda a samu masu zuba jari su shigo kasar ko tattalin arzikinta zai bunkasa.

Ga cikakken rahoton wakiliyar Murya Amurka Medina Dauda.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:32 0:00

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG