WASHINGTON D.C. —
Shugabannin Tarayyar Turai suna fatan majalisar dokokin Birtaniya za ta kada kuri'ar amincewa da sabuwar yarjejeniyar ficewa daga tarayyar turai idan ta zo gaban 'yan majalisar a gobe Asabar, amma tuni jam’iyyun adawa suka ce ba za su amince ba.
Firai Minista Boris Johnson da kungiyar tarayyar turai sun cimma matsaya a safiyar jiya Alhamis, makonni biyu kafin alkawarin da ya yi na ficewa daga tarayyar turai, ko da yarjejeniyar ko babu.
Johnson ya kira sabuwar yarjejeniyar "mai girma" ga Birtaniya, da mutanenta, da kungiyar tarayyar turai.
Sai dai dukkanin jam’iyyun adawar kasar, sun yi fatali da yarjejeniyar ciki har da kawayen Firai Minista Johnson, Northern Ireland Democratic Unionist Movement.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 18, 2021
Kungiyar Kasuwanci ta Duniya Na Bukatar Sabon Salon Gudanarwa-Dr. Ngozi
-
Fabrairu 18, 2021
Guterres Ya Yi Kiran a Samar Da Tsarin Bai Daya Na Rigakafin Coronavirus