Wannan al’amari ya tada hankalin hukumomin Ghana, ganin yadda sashen noma ke taimakawa tattalin arzikin kasar. Hakan ya kai ga daukar muhimman matakai na neman dalilin da ya haddasa rubewar abincin.
A dalilin haka hukumar kula da ingancin kaya ta Ghana tare da taimakon gwamnati Jamus, suka kirkiro cibiyar inganta diyan itace da sauran kayan lambu da za a rika aikewa dasu kasashen waje.
Wasu manoma sun ce gurbacewar kayan gonar ba daga wurinsu bane. Sun gayawa wakilin Sashen Hausa a Ghana cewa masu sarin kayan daga hannunsu ne suka gurbace domin suna amfani da wasu sanadarai dake gurbata abincin.
Facebook Forum