Wata babbar gobara, wadda ta yi kaca-kaca da rukunin gidajen haya a Dhaka babban birniin kasar Bangladesh, ta hallaka mutane akalla 70 a wani sashi mai cike da tarihi.
Gobarar ta tashi ne da daren jiya Laraba a daya daga cikin rukunin gidajen da ke shiyyar Chawkbazar na birnin na Dhaka, kafin ta wanzu cikin lokaci kankani zuwa akalla wasu gine-ginen kuma guda huda.
‘Yan kwana-kwana sun ce akasarin wadanda abin ya rutsa da su sun makale ne cikin gidajen. Akalla wasu mutanen kuma 50 sun ji raunuka.
Facebook Forum