Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

GRACE ALHERI ABDU: Domin Iyali- Garkuwa Da Mata A Jihar Katsina, Kashi Na Biyu-Satumba,19, 2019


Alheri Grace Abdu
Alheri Grace Abdu

Idan kuna biye damu, makon da ya gabata shirin ya yi hira da wadansu a jihar Katsina da ake fama da haren haren 'yan bindiga. 'Yan bindiga sun yi garkuwa da mata da kananan yara a garuruwa da dama da ya hada da garin Shinfida. A cikin hirarmu da daya daga cikin wadanda aka yi garkuwa da iyalinsa wanda muka saya sunansa sabili da dalilan tsaro ya bayyana takaicin gaza iya shawo kan maharan da yace suna da makamai da suka fi na jami'an tsaro da aka tura yankin.

A cikin hirarsu da Shirin Domin Iyali, gwamnan jihar Katsina Aminu Bello Masari ya bayyana cewa gwamnati ta dauki matakin sulhun ne domin ba maharan damar sake shawara su rungumi dabi'ar kwarai amma idan suka ki za a shiga yaki da su sai an ga bayansu baki daya.

Saurari cikakken shirin domin jin abinda al'ummar shinkafi ke cewa game da wannan lamarin da kuma matakan da gwamnatin jihar Katsina ta dauka kawo yanzu.

Garkuwa da mata a jihar Katsina-10:30"
please wait

No media source currently available

0:00 0:10:34 0:00


  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG