Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

GRACE ALHERI ABDU: Domin Iyali, Oktoba 11, 2018: Damawa Da Mata A Harkokin Siyasa, Kashi Na Uku


Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu

Masu kula da lamura kan harkokin siyasar Najeriya sun bayyana cewa, tilas ne jam'iyun siyasa su sake lale, yayinda kuma a nata bangaren ya kamata gwamnati ta kafa dokar da zata tabbatar da cika alkawarin ba mata damar tsayawa takara su kuma shiga a dama da su a gwamnati kamar yadda Najeriya ta amince tare da sa hannu a kudurin da ya bukaci a ba mata kashi talatin da biyar cikin dari na mukaman siyasa.

Domin bibiya kan wannan batun, shirin Domin Iyali ya gayyaci Barrister Badiha Abdullahi Mu'azu 'yar gwaggwarmayar kare hakin bil'adama, da Hajiya Hauwa El-Yakub mai neman tsayawa takarar majalisar dattijai karkashin tutar jam'iyar NPM domin wakiltar mazabar Kano ta tsakiya, da kuma, Kwamred Sa'idu Kabiru Dakata darektan cibiyar wayar da kan al'umma game da shugabanci na gari.

Saurari bayanansu a wannan tattaunawa da wakilin Sashen Hausa Mahmud Ibrahim Kwari ya jagoranta:

Damawa da Mata a siyasa Pt4-10:30"
please wait

No media source currently available

0:00 0:10:28 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG