Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

GRACE ALHERI ABDU: Domin Iyali, Yuni 28, 2018: Bibiya Kan Tsarin Ciyar Da Yara A Makarantun Gwamnatin Najeriya Kashi Na Daya


Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu

yau shirin Domin Iyali ya gayyaci masu ruwa da tsaki domin neman hanyar inganta shirin ciyar da yara da abinci a makarantun gwamnatin Najeriya, inda yanzu haka ake gudanar da shirin a matsayin gwaji a jihohi 24 na kasar da kuma birnin Taraya Abuja.

Masu ruwa da tsaki da shirin ya hallara domin bibiya kan wannan batun da sun hada da

sun kuma tattauna kan yadda shirin yake tafiya, da kalubalai da ake fuskanta, da kuma matakan da za a bi na gyara.Mun kuma nazarci abinda aka yi, da abinda ba a yi ba, da kuma nasarorin da shirin ya cimma da al'amuran da suka jibinci aiwatar da wannan shirin.

Domin nazari a kan wannan batu, shirin ya gayyaci Mallam Sani Rabi'u, shugaban makarantar firamare da Janbulo a birnin Kano, da Kwamred Tahir Mahmud Saleh, babban jami'i a wata kungiya da ake kira Bridge Nigeria Initiative masu rajin bunkasa harkokin ilimi musamman a yankunan karkara, a wadansu jihohin arewacin Najeriya, sai kuma Mallam Abdullahi Ja'afar wanda yake daga cikin rukunin wadanda aka dauka a tsarin wucin gadi don bibiyar yadda al'amuran suke tafiya a wadansu daga cikin makarantun jihar Kano

Ga jagoran tattaunawar Mahmud Ibrahim Kwari da kashi na daya na wannan tattaunawar.

Bibiya Kan Ciyar Da yara da abinci a makarantu-10:25"
please wait

No media source currently available

0:00 0:10:37 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG