Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnan Jihar Neja Ya Kaddamar da Kamfanin Sarafa Shinkafa A Bida


Gwamnan Jihar Neja Alhaji Abubakar Sani Bello
Gwamnan Jihar Neja Alhaji Abubakar Sani Bello

Gwamnatin jihar Neja ta kafa kamfanin sarafa shinkafa da zai taimaka wajen yawaita shinkafar a jihar da ma kasar Najeriya

Yayinda yake zantawa da Muryar Amurka gwamnan jihar Alhaji Abubakar Sani Bello yace an bude sabon kamfanin sarafa shinkafar ne a garin Bida a karkashin wani shirin hadin gwuiwa tsakanin gwamnatocin tarayyar Najeriya da jihar Neja da kasar Koriya.

Gwamnan yace sun bude kamfanin ne saboda yana cikin ayyukan da suka sa gaba zasu yi domin samun sarafa kayan anfanin noma da samar wa jama'a aikin yi.

Kowane awa daya kamfanin zai sarafa shinkafa tan daya da rabi wato cikin awa takwas zai sarafa tan 12 ke nan.

Kamar yadda gwamnan yayi bayani za'a dankawa wani kamfanin da zai dinga gudanar da harkokin sarafa shinkafa. Kamfanin zai dinga sayen shinkafa daga manoma ya sarafa kana ya sayar. Ba za'a bari ya shigo da shinkafa daga waje ba.

Kungiyoyin manoma sun yi maraba da zuwan kamfanin wanda suka ce zai taimaka wajen cigabansu. Alhaji Shehu Galadima shugaban hadaddiyar kungiyar manoma a jihar yace kamfanin zai fadada ayyukan manoma zai kuma kara masu arziki.

Alkalumma sun nuna Najeriya na bukatar shinkafa tan miliyan tara maimakon tan miliyan biyar da yanzu ake samu cikin gida.

Ga rahoton Mustapha Nasiru Batsari da karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:55 0:00

```````````````````````````````````````````````

````````````````````````````````````````````````````````````````````````````````````````````````````````````

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG