Mukaddashin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya ce gwamnati ta na kokarin ganin an kubutar da mutanen da ke hannun 'yan kungiyar Boko Haram da aka kamasu a lokacin da suke binciken albarkatun man fetur a jihar Borno.
Osinbajo ya bayyana hakan ne a lokacin da yake kaddamar da wani kamfanin sarrafa shinkafa a birnin Arugungu da ke jihar Kebbi.
Mukadasshin shugaban kasan ya ce mutanen sun sadaukar da rayukansu domin yi wa kasa aiki saboda haka tsaro da lafiyarsu, ya rataya a wuyan gwamnati.
A makon da ya gabata ne ne 'yan Boko Haram suka yi wa ayarin mutanen masu binciken man fetur daga Jami'ar Maiduguri da ma'aikatan NNPC kwantan-bauna a jihar Borno.
Lamarin ya kai ga asarar rayukan sojojin Najeriya da wasu 'yan sintiri na sa-kai ko kuma 'yan Civian JTF.
Ga rahoton Murta Faruk Sanyinna da karin bayani.
Facebook Forum