Wannan cibiyar itace irinta ta farko a duk fadin nahiyar Afrika Ta Yamma.
Da yake kaddamar da cibiyar, Gwamnan jihar Lagos Akinwumi Ambode yace cibiyar zata taimaka kwarai wajen raba gardama tsakanin ‘yan uwa ko kuma iyaye.
Haka kuma zata taimaka wa ayyukan ‘yan sanda da na shara’a wajen warware shara’oin dake da sarkakiyar mallakar jini ko jinsi.
Karamin Jakadar Amurka dake Lagos, Mr John Brai ya yaba da wannan yunkurin.
Ga Babbangida Jibrin da karin bayani
Facebook Forum