Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnatin Najeriya Zata Sake Nazari Akan Jakadoji 42


Shugaban Najeriya Muhammad Buhari da mataimakinsa Yemi Osinbajo
Shugaban Najeriya Muhammad Buhari da mataimakinsa Yemi Osinbajo

Kakakin shugaban Najeriya Malam Garba Shehu yace shugaban da gwamnatinsa na sake yin nazari akan sunayen jakadoji 42 da a can baya aka mika sunayensu zuwa Majalisar Dattawa domin tantancesu

An samu matsaloli da sunayen ciki har da na rashin amincewar wasu da karbar mukamin kamar yadda Polin Talin tayi saboda rashin lafiyar mijinta.

Malam Garba Shehu yace abu na jama'a dole ne a yi korafe-korafe. Yace an sa ido domin akwai bukatu na gwamnonin jihohi da manyan 'yan siyasa da masu mulki da wadanda suka san abun da aka yi dasu can baya da suke ganin sun isa su sa a yi.

Tunda aka ce mutane arba'in da biyu za'a fitar ba kowa ba ne zai samu yadda ransa yake so ba. Inji Malam Garba Shehu koda an kai sabbin sunaye Majalisar Dattawa za'a sake samun gaddama akansu. Saidai a duba kasar a kyautata domin a cigaba da ayyuka.

Yace a fahimtarsa za'a sake mayarwa Majalisar Dattawa sunayen da aka daidaita domin a tantancesu su tafi su wakilci Najeriya a kasashen waje.

Wani batun da majalisar zartaswa zata yi nazari a kai shi ne na mukaddashin shugaban hukumar EFCC tunda Majalisar Dattawa ta ki amincewa da sunan Ibrahim Magu sanadiyar rahoton tsaro da hukumar DSS ta bayar a kansa.

Ita Majalisar Dattawa tace dole ne ta tantance duk sunan da aka kawo mata saboda haka ba zata yi aiki cikin gaggawa ba, wato a bata suna yau a ce ta amince nan take ba zata yiwu ba.

Ga rahoton Medina Dauda da karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:34 0:00

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG