Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamnatin Tarayya Tayi Taron Gaggawa Kan Rikicin Mambilla A Jahar Taraba.


Mataimakin shugaban Najeriya Yemi Osinbanjo.
Mataimakin shugaban Najeriya Yemi Osinbanjo.

Hafizu Ibrahim hadimin mukaddashin shugaban kasa ne ya bayyana haka, bayan zaman da aka yi kan wannan batu.

Mukaddashin shugaban Najeriya Parfessa Yemi Osinbajo, ya kafa kwamitin bincike kan rikicin Taraba.

Parfessa Osinbajo, yayi ta’aziyya ga iyalan wadanda wannan rikici na tsaunin Mambilla ya shafa.

Babban hadimin mukaddashin shugaban kasa Hamisu Ibrahim, wanda ya bayyana haka, yace Parfessa Osibanjo, ya gana ne da shugabannin hukumomin tsaro tareda Gwamnan jahar Darius Isiyaku, da zummar gano bakin zare.

Da yake sharhi kan yawa-yawan tashe tashen hankula a arewacin kasar, Kabiru Danladi Lawunti, yace rashin hukunta wadanda suke tada wadannan fitintinun shi yasa ake ci gaba da fuskantar. Kamar yadda ake gani a jihohin Kaduna, da Flato, da Nasarawa, da Benue da Taraba.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:48 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG