Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwamtani Kaduna Ta Ce 'Yan Ta'adda Ne Suka Dasa Bama-bamai a Kabala


Jami'in yada labarai da hulda da jama'a na gwamnmatin jihar Kaduna, Samuel Aruwan
Jami'in yada labarai da hulda da jama'a na gwamnmatin jihar Kaduna, Samuel Aruwan

Gwamnatin jahar Kaduna ta ce an auna arziki ne da bama-baman da aka gano an dasa a yankin Kabala-West da Unguwan Romi ba su tashi cikin jama'a ba, amma da an yi asarar rayuka da dukiyoyi.

A maraicen ranar Lahadin da ta gabata ne dai wasu abubuwa da ake zargin bama-bamai ne su ka fashe a yankin Kabala-West da ke Karamar hukumar Kaduna ta Kudu kana daga bisani aka sake gano wasu abubuwan fashewar a yankin Unguwan Romi sai dai an auna arziki saboda ba a yi asarar rayuka ba.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Kaduna, Malam Samuel Aruwan ya ce gwamnatin jihar ta fitar da tsare-tsaren magance wannan matsala baki daya.

Tuni dai masana harkokin tsaro a Najeriya su ka fara nazarin wannan sabuwar matsala da ta fito a Kaduna. Manjo Yahaya Shinko mai ritaya ya ce akwai wasu abubuwan lura.

Wannan dai shine na farko tun bayan zaben wannan gwamnati ta jahar Kaduna a shekarar 2015 da aka sami fashe-fashen da gwamnatin ke ganin 'yan-ta'adda ne sanadi, saboda fashewar baya da aka taba samu a yankin sabon Tasha na masu sana'ar kayan da ke da nasaba da fashewar ne.

Saurari cikakken rahoton cikin sauti:

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00

XS
SM
MD
LG