Watannin ukku yanzu da sa wa dokar kasafin kudi a Nigeria hannu, har yanzu ba fara aikin sake gina jihohin Arewa maso gabashin kasar ba da yaki ya daidaita.
Hakan kuwa ya biyo bayan rashin bada kudin da za’a gudanar da wannan aikin ne daga gwamnatin tarayya.
Shugaban kwamitin kula da wannan aiki na majilisar wakilai, Yusuf Captain Buba yace da zaran an saki kudin, aiki zai kankama duk da yake kudin ba zasu isa ba.
Facebook Forum