Yanzu ana iya cewa jigilar Alhazan Najeriya an sha karfin sa domin yanzu makonni 4 kenan da fara wannan aiki.
Abinda ya dauki hankalin a wannan shekarar shine irin tsarin ciyar da Alhazai da hukumar Alhazan ta Najeriya tayi, wajen tabbatar da kyawon abinci da za a baiwa Alhazan, sabanin irin tsarin da ake yi ada.
A shekarun da suka gabata akan baiwa Alhaji kudin abincin sa a hannun sa ne, kana ya nemi abinda zaici da kansa, amma wannan karon abin yasha ban-ban.
Musali Hajiya Hussaina Abba Yarima ta zo aikin Haji ne daga jihar Nassarawa, kuma ta shaidawa wakiliyar sashen Hausa Madina Dauda cewa.
‘’Shekaru 36 da suka gabata lokacin data yi aikin Hajjin ta na farko, su Alhazai sune suke ciyar da kansu, da dai sauran bukatun su, amma wannan karon da suka zo cinsu da shansu duka a Hotel din da suke zaune ne ke daukar dawainiyar hakan, bayan wurin kwanan su’’.
Ga Dai Madina Dauda da Karin Bayani.
Facebook Forum