‘Yar majalisar na bangarn Democrats, Ilhan Omar wacce take wakiltan wata gunduma a jihar Minnesota dake tsakiya maso yammacin Amurka tsawon makwanni biyar, tace wani rukunin ‘yan Isra’ila mai kamun kafa a nan Amurka, wato kungiyar huldan Amurka da Isra’ila tana sayen ‘yan majalisar domin bada goyon bayansu ga kasar Isra’ila.
Ta yi wadannan kalaman ne a wani sakon Twitter a ranar Asabar, tana mai cewa goyon baya da ‘yan majalisar ke baiwa Isra’ila suna yi ne saboda kudin dake fitowa kungiyar AIPAC mai kare akidojin Yahudawa, koda yake kungiyar bata taiamakawa yakin neman zaben ‘yan siayasar Amurka kai tsaye, amma kuma mambobinta zasu iya taimakawa.
Facebook Forum