Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Illar Coronavirus Ga Tattalin Arzikin Najeriya


Lagos
Lagos

Najeriya ta sassauta dokar hana fita saboda coronavirus ne domin rage barnar da take yiwa tattalin arzikin kasar.

Matakin da aka dauka a ranar Litinin na zuwa ne bayan kwashe makwanni da rufe harkoki a fadin kasar wanda ya yiwa miliyoyin kasuwanci illa.

Najeriya ta sassauta dokar hana fita ta kwanaki 35 ne a Abuja da Legas da Ogun, bayan umarnin shugaba Muhammadu Buhari a makon da ya gabata a wani jawabi da ya yiwa kasar.

Shugaba Buhari ya yarda cewa hana mutane gudanar da ayyuka ya yi illa ga tattalin arzikin Najeriya, musamman a bangare kananan ayyuka da sai an yi su a kullum.

Sai dai shawarar sassauta dokar hana fitan na zuwa ne a lokacin da ake kara samun masu kamuwa da cutar coronavirus.

Alkaluman da cibiyar yaki da cututtuka masu yaduwa ta Najeriya NCDC ta fitar adadin ya ninka a makon da ya gabata, inda mutane sama da dubu biyu da dari biyar suka kamu ya zuwa ranar Litinin.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG