Haka ita ma Turkiyya tace zata bada gudumawar abinci ga Qatar, yayinda suke fargabar kasar zata iya fuskantar karancin abinci, bayan da Saudiyya ta rufe kan iyakarta da kasar Qatar, iyakar kasar guda daya a doron kasa, wacce take amfani d a shi wajen sayo galibin kayayyakin abincin da take bukata.
A makon jiya ne kasashen Saudiyya, da hadaddiyar daular kasashen larabawa, da Bharain, da Masar suka tsinka huldar jakadanci da Qatar, suna zargin 'yar karamar kasar da goyon bayan mayakan sa kai masu ikirarin Islama, da kuma Iran, zargin da Qatar tace bashi da tushe. Shugaban Amurka Donald Trump, shima ya zargi Qatar da kakkausar lafazi.
Facebook Forum