Bayan da Amurka ta kai wani hari da ya yi sanadiyyar mutuwar kwamandan zaratan sojojin juyin juya hali na Qud, Oassem Soleimani, Iran ta sha alwashin mayar da martani.
Ministan Harkokin Wajen Iran, Mohammad Javad Zarif, ya kira kisan Janar din a matsayin keta 'yancin Iran da kuma aikata harin ta’addanci akan kasar.
Duk da dai cewar ma’akatar tsaro ta Amurka ta kare harin in da ta cewa, Janar din na da niyyar kai hare-hare kan jami’an diplomasiyya da ke Iran, shi dai shugaban Iran Hassan Rouhani ya ce, "tabbas, ba shakka, Iran da sauran kasashen duniya za su mayar da martani.”
Ita kuwa, Shugabar Majalisar Wakilan Amurka, Nancy Pelosi, ta yi Allah wadai da harin inda ta ce an kai shi ne ba tare da tuntubar majalisar ba.
Kuma a cewarta, wannan harin zai iya janyo karin rikice-rikice wadanda ba a bukata yanzu a duk fadin Duniya.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 18, 2021
Kungiyar Kasuwanci ta Duniya Na Bukatar Sabon Salon Gudanarwa-Dr. Ngozi
-
Fabrairu 18, 2021
Guterres Ya Yi Kiran a Samar Da Tsarin Bai Daya Na Rigakafin Coronavirus
-
Fabrairu 16, 2021
Kungiyar WTO Ta Gabatar Da Sabuwar Shugaba Ngozi Okonjo-Iweala
-
Fabrairu 16, 2021
Hukumar Lafiya Ta Duniya (WHO) Ta Aminta Da Riga Kafin AstraZeneca
Facebook Forum