A yau Asabar jami’an Afghanistan suka sanar da cewa jami’an tsaro sun sake kwato wata muhimmiyar gunduma a arewa maso gabashin kasar daga hannun ‘yan Taliban bayan shekaru 5, a yayinda ake ci gaba da gwabza kazamin fada a wasu lardunan Afghanistan.
Kungiyar Taliban ta kara zafafa hare-haren ta duk da cewa wakilan kungiyar sun sake hawa kan teburin shawarwari da Amurka a Qatar don kawo karshen yakin na Afghanistan wanda aka kwashe shekaru 18 ana yi, wannan shine yaki mafi tsawo da Amurka ta shiga a wata kasar.
Ma’aikatar tsaron Afghanistan ta ce fadan da aka yi don kwato garin Wardoj a lardin Badakhshan yayi sanadiyar mutuwar kusan ‘yan kungiyar Taliban 100, ciki har da manyan kwamandojinsu. Ma’aikatar ta yi ikirarin cewa jami’an tsaron Afghanistan ne suka kai hare-haren ba tare da yin hasarar rai ko daya ba.
Lardin Badakhshan dai ya hada iyaka da kasashe makwabtan Afghanistan guda 3, ciki harda China, da Pakistan da kuma Tajikistan.
Za ku iya son wannan ma
-
Maris 29, 2023
Ukraine Ta Kaiwa Rasha Wani Mummunan Hari
-
Maris 29, 2023
Kasar Azerbaijan Ta kaddamar Da Binciken Harin 'Yan Ta'adda
Facebook Forum