Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jam’iyyar APC Ta Lashe Zaben Gwamnan Jihar Ekiti


Tambarin hukumar zaben Najeriya.
Tambarin hukumar zaben Najeriya.

Dan takarar gwamna na jam’iyyar APC Dakta Kayode Fayemi, ya lashe zaben jihar Ekiti da aka gudanar ranar Asabar.

Da yake bayyana sakamakon zaben Farfesa Idowu Olayinka, ya bayyana cewa Dakta Kayode Fayemi ya lashe zaben jihar Ekiti da kuri’u 197,459 shi kuma abokin takarar na jam’iyyar PDP ya samu kuri’u 178,471.

Dakta Fayemi yana kan gaba ne a kananan hukumoni 12 cikin 16 na jihar, shi kuma abokin takararsa yana kan gaba a sauran kananan hukumomi hudu.

Wasu daga cikin ‘yan jihar Ekiti sun bayyanawa Muryar Amurka farin cikinsu game da yadda aka gudanar da zaben cikin gaskiya da kwanciyar hankali.

Muryar Amurka ta yi kokari jin ta bakin ‘yan jam’iyyar PDP amma hakka bata cimma ruwa ba, domin duk wanda aka tuntuba yana mai cewa ba zai iya cewa komai ba a halin yanzu.

Domin karin bayani saurari rahotan Hassan Umaru Tambuwal.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:08 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG