Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jimillar Wadanda Suka Kamu Da COVID-19 a Najeriya Ta Doshi 40,000


Jami'an Gwaijn COVID-19
Jami'an Gwaijn COVID-19

Hukumar NCDC mai kula da cututtuka masu yaduwa a Najeriya ta ce an samu karin mutum 591 da suka kamu da cutar COVID-19 a ranar Juma’a 24 ga watan Yuli.

A sanarwar da ta fidda a shafinta Twitter a daren ranar Juma’a, hukumar ta ce jihar Oyo ta samu karin mutum 191 yayin da jihar Lagos da ke kan gaba a yawan wadanda suka kamu da cutar a fadin kasar ta samu mutum 168.

Sauran jihohin sun hada da birnin tarayya Abuja inda aka samu mutum 61, sai Ondo 29, 26 a Osun, 24 a Ebonyi, 23 a Edo, 14 a Ogun, 13 a Rivers, 12 a Akwa Ibom, 10 a Kaduna, 6 a Katsina, 4 a Borno. Jihohin Delta, Ekiti da Imo kuma mutum 3 kowannensu, sai kuma 1 a Niger.

Gaba dayan adadin wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar yanzu ya kai 39,539, an kuma sallami mutum 16,559 bayan haka mutum 845 suka mutu.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG