Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kamaru: Daruruwan Mayakan Boko Haram Na Mika Wuya Bayan Mutuwar Abubakar Shekau


Hukumomi a Kamaru sun ce suna samun karuwar mayakan Boko Haram da ke mika kansu a wata cibiyar kwance damarar makamai da ke kan iyakar arewancin kasar da Najeriya.

Jami'ai sun ce akwai daruruwan sauye-sauye daga kungiyar 'yan ta'addan tun daga watan Mayu, lokacin da aka bayyana mutuwar Abubakar Shekau, shugaban kungiyar.

Hukumomin Kamaru sun ce adadin masu tubban wadanda suka tsere daga kungiyar masu tsattsauran ra'ayi na Boko Haram ya fi karfin su.

Kwamitin kasa na kwance damarar yaki da raba makamai da sake hadewa, ko kuma DDR, wanda cibiyar gwamnati ta kafa, ta dauki bakuncin tsoffin mayaka 750 a Meri, wani gari da ke kan iyakar arewancin Kamaru da Najeriya.

Dieudonne Nkollo Zanga na ɗaya daga cikin masu gudanar da cibiyar DDR a Meri. Ya ce cibiyar ta karbi mayaka sama da 155 a cikin kwanaki bakwai da suka gabata kuma jimillar mayakan kimanin 450 sun isa cibiyar tun daga watan Mayu.

Zanga ya ce cibiyar a Meri karama ce kuma ba za ta iya karbar karuwar adadin mayakan Boko Haram da ke barin kungiyar ba. Jami'an DDR sun ce galibin mayakan 155 da suka isa wannan makon matan mayakan ne da 'ya'yansu. Arba'in daga cikin mutanen 57 tsoffin mayakan Boko Haram ne.

Francis Fai Yengo darakta ne na cibiyar DDR ta gwamnati. Ya fadawa manema labarai jiya litinin cewa gwamnati ta dauki matakan da suka dace don biyan bukatun tsoffin mayakan. Da yake magana a wani taron manema labarai a Yaounde, Yengo ya ce shugaban Kamaru, Paul Biya, ya umarci jami'ai da su yi afuwa ga duk mayakan da suka mika wuya da kuma kwance damarar makamai.

Ya ce galibin mayakan da ke tserewa daga daji don shiga cibiyar DDR na bukatar taimako daga gubar amfani da kayan maye.

Ya kara da cewa, yana da matukar wahala a iya taimaka wa tsoffin mayakan Boko Haram muddin mayakan na ci gaba da fama da matsalar amfani da kayan maye.

Saibou Issa kwararre ne kan warware rikice -rikice a Jami'ar Maroua ta Kamaru kuma a cewarsa, mayakan da yawa suna ficewa bayan mutuwar Abubakar Shekau, shugaban Boko Haram, a watan Mayu.

Issa ya ce hare-haren da rundunar hadin gwiwa ta kai a yankunan da ke karkashin ikon Boko Haram da mayakan sa sun raunana mayakan na Shekau.

XS
SM
MD
LG