Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kasar Koriya ta Arewa Matsala Ce Dole Na Maganceta - Donald Trump


Shugaban Amurka Donald Trump da Firayim Ministan Canada Justin Trudeau
Shugaban Amurka Donald Trump da Firayim Ministan Canada Justin Trudeau

Yayinda yake karban bakuncin Firayim Ministan kasar Canada Shugaban Amurka Donald Trump yace kasar Koriya ta Arewa matsala ce da dole sai ya maganceta wa Amurka da duniya

A jiya Laraba ne shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana Koriya ta Arewa a matsayin “matsalar da dole sai anyi maganinta.”

A lokacin da shugaba yake tare da Faray Ministan Canada, Justin Trudeau, a ofishinsa dake fadar White House, Trump ya ce “Tabbas, zanyi abin da ya dace ga Amurka, da kuma abin da ya dace ga duniya baki daya.”

A halin yanzu kuma, ministan harkokin wajen Koriya ta Arewa, Ri Yong Ho,ya zargi shugaba Trump da cewa shine ya soma kunna wutar tsokanar janyo yaki a yankunan Koriya, bayan da yayi baraznar cewa Amurka zata ruguza Koriya ta Arewa idan har ta kai mata hari.

Trump dai yayi wannan barazanar ne a lokacin da yake jawabi a gaban babban taron shugabannin kasashen duniya a zauren MDD a watan da ya gabata.

A daidai lokacinda shugaban na Amurka ketunanin amfani da karfin soja kan Koriya ta Arewa, sojojin Amurka da Japan dana Koriya ta Kudu, sun gudanar da wani atisaye don tsoratar da Koriya ta Arewa, inda suka yi ta harba makamai masu linzami daga gabashi da kuma yammacin gabar zirin koriya a ranar Talatar shekaranjiya.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG