Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kasar Saudiyya Ta Zargi Kasar Iran da Takalarta da Yaki


Sarkin Saudiyya Salman a tsakiyan ministan tattalin arziki da na hukumar tsaron kasar

A cewar kasar Saudiyya makami mai linzami da 'yan tawayen Houthi dake samun goyon bayan Iran suka harba akan birnin Riyadh tamkar takala ce ta yaki Iran ta yi

Saudiyya ta ce kasar Iran tayi abinda ta kira “takalar yaki” lokacin da ‘yan tawayen Houthi da Iran din ke marawa baya a Yamal suka harba makami mai linzami akan birnin Riyadh.

Saudi dai ta tare makami mai linzamin da aka harba filin jiragen saman King Khalid ranar Asabar.

Sojojin kawance na hadin gwiwa dake yakar ‘yan Houthi da Saudi ke jagoranta, ta ce tana da ikon mayar da martanin soja kan abin da Iran ta yi.

Ministan harkokin wajen Saudiyya Adel al-Jubeir, ya fada a shafinsa na Twitter cewa “katsalandan din da Iran take a yankin, na kawo barazana ga makwaptan kasashe, yana kuma shafar zaman lafiya da tsaro.”

Iran ta musanta cewa tana baiwa ‘yan tawayen Houthi makamai, kuma ministan harkokin wajen Iran din Mohammed Javad Zarif ya caccaki Saudiyya, kan zama sanadiyar asarar rayuka da rasahin zaman lafiya a Yamal.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG