Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kasashen Afrika Na Ci Gaba Da Jajen Rasuwar Kofi Anan


Kofi Anan
Kofi Anan

Jama’ar jamhuriyar Nijer sun nuna juyayi akan rasuwar tsohon sakataren majalisar dinkin duniya Kofi Anan wanda Allah ya yiwa cikawa a shekaranjiya asabar. Suna masu yiwa marigayin kyaukyawar shaida saboda gudunmuwar da ya baya a fannoni da dama.

Sadaukar da kai akan batun zaman lafiya na daga cikin halayyar da a yau ke ja wa marigayi Kofi Anan kyakyawar shaida daga jama’a bisa la’akari da yadda ya dage haikan wajen jawon hankalin shuwagabanin duniya kan mahimmancin warware rikici ta hanyar sulhu a maimakon amfani da karfin soja. Alkassimu Abdurrahman wani mai sharhi akan al’amuran yau da kullum yace abubuwan da suka faru a yankunan Serbia, lokuta ne da majalisar dinkin duniya ta fuskanci barazana kuma duka lokutan da Kofi Anan ke jagoranci ne, shiyasa ake ganin yayi kokari.

Haka shi ma Alh. Salissou Amadou wani dan rajin kare demokradiya ya bayyana shugabannincin Kofi Anan a matsayin wanda ya gudana cikin hikima da kwarewa ya kara da cewa yana daka cikin

Kofi Anan ya ziyarci jamhuriyar Nijer a shekarar 2005 a wani lokacin da kasar ke fama da karancin abinci inda ya yi amfani da matsayinsa na sakataren Majalisar Dinkin Duniya domin jan hankulan kasashen duniya su kai daukin cimaka wa jama’ar wannan kasa.

Sauri cikakken rahoton Souley Moumouni Barma

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:32 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG