Sakar wa mata ragamar samun matsayin shugabanci ta hanyar zabe ko nade-nade na cikin alkawurran da Kungiyar Bunkasa tattalin Azriki ta Kasashen Afrika ta Yamma, ECOWAS, suka yi tun a shekarar 2015, amma har yanzu yawancinsu basu cika alkawarin ba.
Kan hakan ne, Kungiyar ta shirya taron duba matsalar a Junhuriyar Nijar domin binciken dalilin da ya sa aka samu tsaiko wajen cika alkawarin.
Sani Bukari, shugaban tawagar Nijar a wajen taron, yace gane cewa rayuwa sai da mata, shi yassa suka taron don a ga yadda za’a iya cika alkawarin da aka yiwa matan.
Ministar cigaban mata da bayar da kariya ga yara ta Nijar, Madam Zainabu Tari Bako, ta jinjinawa ECOWAS akan wannan yunkurin da tace yana da alfanu ga cigaban alumma.
Ga Souley Moumouni Barma da karin bayani.
Facebook Forum