Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kasuwar ‘Yan Doya ta Garin Tagina, Jihar Neja


Shirin kasuwa na wannan makon ya kai ziyara kasuwar ‘yan doya a garin Tagina da ke karamar hukumar Rafi a jihar Neja, Najeriya.

Wakilin Muryar Amurka Mustapha Nasiru Batsari, ya yi hira da masu saye da sayarwa a kasuwar da kuma yanayin sana’ar baki daya.

Ayuba Auta, shi ne sarkin kasuwar doya ta garin Tagina, ya ce an sami ci gaba musamman ganin yadda doya ta yi daraja a bana kuma ana samun masu saye, duk da cewa farashinta ya hau.

Hakazalika wasu ‘yan kasuwar su ma sun shaida cewa an sami ci gaba a kasuwar, sai dai babbar matsalarsu ita ce rashin rumfuna.

Saurari cikakken shirin cikin sauti.

Kasuwar ‘Yan Doya ta Garin Tagina, Jihar Neja
please wait

No media source currently available

0:00 0:09:59 0:00


XS
SM
MD
LG