Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kira ga Najeriya Tayi Koyi ga Kasashen da Suka Cigaba a Zaben da Za’ayi


Shugaban Hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya, (INEC) Attahiru Jega.
Shugaban Hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya, (INEC) Attahiru Jega.

Shugaban hukumar zaben Najeriya Prof. Attahiru Jega, yayi kira ga ‘yan siyasar Najeriya da suyi koyi da takwarorinsu na Amurka wadanda basa siyasar ko a mutu ko a yi rai.

Prof. Jega ya bada wannan shawarar ce lokacin da ya ziyarci sashen Hausa na Muryar Amurka, bayan da ya kalli yadda aka gudanar da zaben rabin wa’adi na nan Amurka a makon jiya.

‘yan siyasar Najeriya dai ko kuma masu mulkin kasar, na amfani da madafun mulkin su wajen dauwama akan mulki ko nasara akan zabe, Pro. Jega dai yace wannan matsala ce tunda yake duk wanda ya dandana mulki bayaso ya bari, kuma duk yadda zaiyi ya cigaba to sai yayi.

Saurari hirar Pro. Jega da Sahabo Imam Aliyu.

please wait

No media source currently available

0:00 0:04:34 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG