Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kisa Da Sace Mutane: An Hana Hakar Ma’adanai a Zamfara


SUFETO JANAR MOHAMMED ADAMU ABUBAKAR
SUFETO JANAR MOHAMMED ADAMU ABUBAKAR

Matsalar tsaron Zamfara ta dau wani sabon salo bayan da rundunar 'yan sandan Najeriya ta soke takardar izinin hakar ma'adanai a jahar ta kowa da kowa tare kuma da gaya ma 'yan kasashen waje da ke hakar ma'adanai a jahar su san inda dare ya masu.

A wani bangare na kokarin kawo karshen yawan kashewa da kuma sace mutane a jahar Zamfara, Sufeto-Janar na ‘yansandan Najeriya Mohammed Abubakar Adamu ya dakatar da hakar ma’adanai a jahar Zamfara da kuma duk wani abin da ya shafi harkar hako ma’adanai a jahar da kewaye. Sannan ya bayar da wa’adi ma duk wani dan kasar waje ke harkar hakar ma’adanai a Zamfara da ya tattara ya nasa ya yi gaba.

Wani kwararren kan harkokin yau da kullum mai suna Malam Yusha’u Aliyu, y ace ba a taba samun alaka tsakanin harkar hako ma’adanai a Najeriya da harkar ta’addanci ba. Ya ce akwai alaka ta jari hujja tsakanin masu hakar ma’adanai da masu saye da kuma ma’aikatan saboda haka babu yadda wani bangare zai so a karkashe talakawa masu aiklin ma’adanai. Ya kara da cewa a jahar Filato an jima ana hakar ma’adanai ba tare da an fuskanci irin abin da ke faruwa a Zamfara ba. Y ace akwai ma’adananmu a wasu sassan arewa amma ciki har da Kaduna da kuma Nasarawa amma, kamar yadda abin yak e a jahar Filato, ba a taba ganin masifa irin ta Zamfara a jahohin ba.

To amma wani masanin tsaro, Air Commodore Baba Gamawa (murabus) y ace ruwa baya tsami banza, bas hi yiwuwa bangaren tsaro ya dau irin wannan matakin ba tare da ya ga wasu bayanan sirri ba, wadanda, a cewarsa, ba lallai a bayyana ma sauran jama’a ba.

Da wakilinmu Hassan Maina Kaina da cikakken rahoton:

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG