Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ko Wace Jam'iyya Ce Zata Lashe Zaben Sipaniya?


'Yan kasar Sipaniya sun kada kuri jiya Lahadi, a zaben kasar na hudu a cikin shekaru hudu.

Ana sa ran Firaiminista Pedro Sanchez na jam’iyyar gurguzu ya lashe zaben, kamar yadda ta faru a zaben da ya gabata.

A jawabinsa wajen wani gagarumin yakin neman zabe, Firaiministan yace, "a yau kuri’a ce za ta yi aiki wajen zaben shugabancin Sipaniya a gobe. Babban muhimmin al’amari shine yin kira ga ‘yan kasar Sipaniya da su yi zabe, da kuma karfafa dimokaradiyyar kasar ta hanyar zaben"

Yakin neman zaben da ya kai da zaben na ranar Lahadi, ya maida hankali ne akan yunkurin samun ballewa da ‘yancin kasar Catalonia, da kuma fargabar habakar jam’iyyar Vox.

A zaben da ya gabata, jam’iyyar shugaban na Spaniya ta kasa lashe isassun kuri’un da za su ba ta damar kafa tsayayyar gwamnatin.

Jam’iyyar Vox ce dai ya kamata ta kasance abokiyar hadakar jam’iyyar ‘yan gurguzu da ke mulki, to amma babu jituwa a tsakaninsu, bayan zaman tattaunawa da dama da ba su yi nasara ba, biyo bayan zaben watan Afrilu, da kuma rashin babbar damar samun kuri’un da za su kafa gwamnatin tare.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG