Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Koriya Ta Arewa Ta Koma Bakin Aikin Gina Gurin Gwada Makami Mai Linzamin


Wasu rahotanni sun ce Koriya ta Arewa ta sake komawa bakin aikin gina gurin gwada makami mai linzamin, a cewar wasu cibiyoyin bincike na Koriya Ta Kudu da Amurka.

A yau Laraba Kamfanin Dillancin labarai na Yonhap na Koriya ta Kudu ya ce, ma'aikatan leken asiri sun sanar da mahukunta a wani taron sirri da aka yi cewa, an soma wannan aikin.

Cibiyar Nazarin Harkokin waje ta C.S.I.S. dake Washington ta bayar da rahoto a jiya Talata cewa, Koriya ta Arewa na "ci gaba da sake gina" sansanoninta na kera makamashin nukiliya dake a Sohae, kamar yadda wani hoto da tauraron dan Adam ya dauka tsakanin 16 ga watan Fabrairu zuwa 2 ga watan Maris na wannan shekarar ta 2019.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG