Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Koriya ta Arewa Ta Soke Shirin Tattaunawa Da Koriya ta Kudu


Shugaban Koriya ta Arewa da shugaban Koriya ta Kudu
Shugaban Koriya ta Arewa da shugaban Koriya ta Kudu

Saboda atisayin da sojojin Amurka da na Koriya ta Kudu keyi a zirin Koriya, shugaban Koriya ta Arewa ya soke shirin tattaunawa da Koriya ta Kudu tare da yin barazanar janyewa daga tattaunawar da zai yi da shugaban Amurka watan gobe

Koriya Ta Arewa ta soke muhimmiyar tattaunawar da aka shirya cewa za ta yi jiya Laraba da Koriya Ta Kudu, sannan ta ce ya rage ga Amurka ta kula da makomar ganawar da za a yi tsakanin Shugaba Kim Jong Un da kuma Shugaba Donald Trump saboda atisayen hadin gwiwa tsakanin Koriya Ta Kudu da Amurkar.

Kamfanin Dillancin Labaran Koriya Ta Arewa ya ce atisayen, mai lakabin “Max Thunder” ba wani abu ba ne illa koyon dabarun mamaye Koriya Ta Arewa da kuma takala duk kuwa da irin cigaban da aka samu a dangantakar Koriya Ta Arewa da Koriya Ta Kudu.

Fadar Shugaban Amurka ta White House dai ba ta yi magana sosai ba illa kawai cewa da ta yi za ta cigaba da tattaunawa da kawayenta.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG