Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kotu A Kasar Ivorycost Ta Wanke Simone Gbagbo


Jiya Talata wata Kotu a Ivory Cost ta wanke Simone Gbagbo, matar toshon Shugaban Ivory Coast, wadda aka zarga da laifin cin zarafin bil adama a tashin hankalin bayan zaben 2011.

Ita dai Simone Gbagbo, ba ta a kotun lokacin da aka yanke hukuncin. Masu gabatar da kara na da kwanaki 60 na daukaka kara. Su na bukatar a yanke mata hukuncin daurin rai da rai.

An zargi Simone da jagorantar wata kungiya ta kai hare-hare kan masu adawa da mijinta, tsohon Shugaban kasa Laurent Gbagbo, ciki har da samar da makamai da jirage masu saukar ungulu ma kungiyar.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG