Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kotu Ta Sa A Tsare Alhassan Ado Doguwa A Gidan Yari


Alhassan Ado Doguwa lokacin da jami'an hukumar gyara hali za su kai shi gidan gyara hali
Alhassan Ado Doguwa lokacin da jami'an hukumar gyara hali za su kai shi gidan gyara hali

A zaman farko na ranar Laraba, alkalin kotun ya dage sauraren karar zuwa ranar 7 ga wannan watan nan na Maris.

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano a arewa maso yammacin Najeriya ta gurfanar da shugaban majalisar wakilan kasar Alhassan Ado Doguwa a gaban kotun majistire ta jihar.

Ana tuhumar Doguwa da hannu a tarzomar zabe, inda wasu mutane uku suka rasa rayukansu a yankin mazabarsa.

Alkalin kotun mai shari’a Ibrahim Mansur Yola ya ba da umurnin tsare Alhassan Ado a gidan kurkuku ko cibiyar gyaran hali ta Goron Dutse da ke birnin Kano.

Daga bisani, alkalin ya dage saurarn karar zuwa ranar 7 ga wannan wata na Maris lokacin da kawo batun neman a ba da shi beli.

A shekaranjiya litinin ne tarzoma ta barke a garin Tudunwada tsakanin magoya bayan jam’iyyun APC da NNPP, al’amarin da yayi sanadiyyar mutane akalla uku yayin da wasu da dama suka jikkata.

XS
SM
MD
LG