Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kotun Daukaka Kara Ta Jaddada Hukuncin Kisa Da Aka Yankewa Maryam Sanda 


Maryam Sanda
Maryam Sanda

Kotun daukaka kara da ke Abuja, babban birnin Najeriya, ta tabbatar da hukuncin da aka yankewa Maryam Sanda na kisa ta hanyar rataya bayan da aka same ta da laifin kisan kai.

A farkon shekarar nan babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yankewa Maryam hukuncin kisa bayan da ta same ta da laifin kashe mijinta Bilyaminu Bello, da ga tsohon shugaban jam’iyyar PDP a Najeriya.

Alkalan kotun uku da suka yanke hukuncin a ranar Juma'a, sun ce hujjojin da Maryam ta gabatar na kare kanta ba su da tushe balle makama, abin da suka ce ya zama dole a yi adalci.

Hujjoji da bayanai da aka gabatar a gaban kotun sun nuna cewa Maryam ce ta yi ajalin mijinta a shekarar 2017 ta hanyar caka masa wuka bayan da ma'auratan biyu suka samu sabani.

Ita dai Maryam wacce take da ‘ya’ya biyu da marigayin, ta ce Bilyaminu ya fada ne akan tukunyar shisha lamarin da ya yi sanadin mutuwarsa.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito lauyoyin Maryam suna cewa za su daukaka kara zuwa kotun kolin kasar.

XS
SM
MD
LG