Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kotun Kolin Najeriya Ta Yi Watsi da bukatar PDP na gabatar da sabbin hujojji


Zaman Kotu
Zaman Kotu

Kotun kolin Najeriya ta yi watsi da bukatar da dan takarar shugaban kasa karkashin Inuwar Jam’iyyar PDP yayi na gabatar da sabbin hujojji a gaban ta.

Kotun kolin ta bayana hakan ne a yayin zaman sauraron karar a ranar Alhamis, inda ta ce karbar sabbin hujojji ya sabawa kundin tsarin mülkin kaşar na shekarar 1999 kamar yadda aka yi mata garambawul.

Zaman Kotu
Zaman Kotu

Kotun ta kalubalanci jam’iyyar PDP a kan me ya hana ta mika sabbin hujojjin a cikin wa’adin kwanakin da doka ta tanadar, kama daga kwanakin shigar da kara 21 zuwa kwanaki 190 na sauraron kararrakin zaben shugaban kasa.

Zaman Kotu
Zaman Kotu

A cewar kotun, kamata ya yi jam’iyyar PDP ta shigar da kara a kan zargin takardun bogi tun shekarar 2022 zuwa watan Maris na shekarar 2023.

Ta kara da cewa ba za ta saurari bukatun kara duk wasu korafe-korafe ko shaidu da ba’a gabatar wa kananan kotunan baya ba.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG