WASHINGTON, DC —
WASHINGTON, D.C - Wakiliyar Muryar Amurka a can Abuja, Heather Murdock ta bada labarin cewa har yanzu dai ana kokarin share wannan guba, amma kungiyar ta Doctors tace lokaci na kurewa saboda damuna na zuwa.
Kafin a fara yi wa yaran da gubar ta shafa magani, dole sai an tsaftace kasar da suke takawa da wasa, idan ko ba haka ba, zasu sake kamuwa da cutar.
Yanzu dai an share shekaru 3 bayan barkewar cutar gubar dalma mafi muni a duniya, ya faru a can arewa maso yammacin Najeriya, kuma yanzu ana cigaba da tsaftace kauyukan da ake tunanin sunfi fuskantar hadari, ta yin amfani da wani fasali mai suna “remediation”.
Wannan fasali dai ya kumshi cire gurbatacciyar kasa, da sauya ta da kasa mai kyau. Amma ruwan sama na cigaba da zuba a wannan waje, kuma shugaban kungiyar Doctors without Borders a Najeriya Simon Tyler yace idan ruwan sama ya cigaba da zuba, to watakila dole ne a dakatar da aikin tsaftace kasar, saboda wahalar aiki da kasa da tabo.
Daruruwan yara ne a wannan yanki suka mutu bayan kamuwa da cutar gubar dalma, sannan wasu da yawa kuma sun samu nakasa na tsawon rayuwarsu.
Kafin a fara yi wa yaran da gubar ta shafa magani, dole sai an tsaftace kasar da suke takawa da wasa, idan ko ba haka ba, zasu sake kamuwa da cutar.
Yanzu dai an share shekaru 3 bayan barkewar cutar gubar dalma mafi muni a duniya, ya faru a can arewa maso yammacin Najeriya, kuma yanzu ana cigaba da tsaftace kauyukan da ake tunanin sunfi fuskantar hadari, ta yin amfani da wani fasali mai suna “remediation”.
Wannan fasali dai ya kumshi cire gurbatacciyar kasa, da sauya ta da kasa mai kyau. Amma ruwan sama na cigaba da zuba a wannan waje, kuma shugaban kungiyar Doctors without Borders a Najeriya Simon Tyler yace idan ruwan sama ya cigaba da zuba, to watakila dole ne a dakatar da aikin tsaftace kasar, saboda wahalar aiki da kasa da tabo.
Daruruwan yara ne a wannan yanki suka mutu bayan kamuwa da cutar gubar dalma, sannan wasu da yawa kuma sun samu nakasa na tsawon rayuwarsu.