Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kungiyar Kare Hakkin Bil Adama Ta Ce An Tafka Laifukan Yaki A Libiya


Kungiyar kare hakkin bil Adama ta Amnesty International, ta ce tana da hujjoji da suka nuna cewa bangarorin da ke takaddama da juna a kokarin karbe ikon Tripoli, babban birnin Libya sun tafka laifukan yaki.

Wani rahoto da kungiyar ta Amnesty mai hedkwata a London ta fitar a jiya Talata, ya nuna cewa mayakan sa-kai sun kashe fararen hula da dama tare da raunata wasu, ta hanyar kai hare-hare.

Kungiyar ta ce ta tattara wadannan bayanai ne a binciken da ta gudanar a yankunan da ake tafka fada, tun bayan barkewar rikici a ranar hudu ga watan Afrilu, inda tawagarta ta ziyarci wurare 33 da aka kai hare-haren sama da na kasa, ta zanta da shaidu.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG