Kungiyar mayakan Hamas dake iko a zirin Gaza ta dauki mataki yau lahadi na kawo karshen takun saka da sabanin siyasa da kungiyar Fatah ta shugaban yankin Palasdinawa Mahmoud Abbas, inda ta amince da rusa majalisar gudanarwarta, da gudanar da babban zabe.
Yayinda tattalin arzikin zirin Gaza ya ruguje, samun wutar lantarki kuma ya koma sa’oi hudu a wuni, kungiyar Hamas tace zata kyale gwamnatin hadin kai ta shugaba Abbas ta yi jaroganci ba tare da bata lokaci ba. An kafa gwamnatin hadin gwiwar ne shekaru uku da suka shige, amma bata sami ikon gudanar da mulki ba a Zirin Gaza sai yanzu.
An sami wannan ci gaban ne bayan zaman tattaunawa dabam dabam da wakilan kungiyoyiyin Hamas da Fatah suka yi da jami’an leken asirin kasar Misira a birnin alkahira.
Mahmoud Aloul, wani jami’n Fatah ya yi na’am da yarjejeniyar, sai dai ya shaidawa wata tashar radiyon Palesdinawa cewa, “muna so mu gani a kasa kafin mu dauki mataki na gaba”.
Facebook Forum