Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kungiyoyin Fafutuka Sun yi Kira Game da Matsalolin ‘Yan Gudun Hijira


'Yan gudun Hijira
'Yan gudun Hijira

Kungiyoyin fafatuka a Najeriya sun yi kira da a gaggauta tabbatar da daftarin shirin kasa a kan yan gudun hijira na cikin gida wato IDP don ya zama doka ta yadda za’a magance matsalolin da ‘yan gudun hijiran ke huskanta.

Kungiyoyin sun bayyana wannan bukatar ne a wajen wani taron tuntuba da Cibiyar Sa-ido Kan Harkokin Majalisu (CISLAC) tare da hadin gwiwar Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya (UNHCR) da kuma ofishin jakadancin kasar Switzerland suka shirya.

Haka kuma mahalarta taron sun yi dubi game da matsalolin rashin samun cikakkun bayanai daga hukumomin da nauyin kula da ‘yan gudun hijira ya rataya a wuyansu, musamman idan ya shafi badakala ko kuma cin zarafi.

Mr Okeke Anya dake zama Daraktan Sha’anin Harkokin Gwamnati na Cibiyar ta CISLAC, yace rashin samar da dokoki da kuma bayanai na cikin kalubalan dake hana ruwa gudu na magance wasu matsalolin da ‘yan gudun hijira ke huskanta.

Ibrahim Abdul’aziz na dauke da karin haske kan taron:

please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:06:15 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG