Hajiya Asma’u Joda memba ce a kwamitin,tace kwamitin zai kuma taimakawa jama’a da jari da ma bunkasa harkokin noma a yankin .
Shiko dan majalisar wakilai mai wakiltar kananan hukumomin Michika da Madagali a majalisar wakilai Mr Adamu Kamale,yace ba su ji na- hutu ba,har sai lokacin da aka kwo karshen matsalolin da suka yiwa yankin kaka-gida.
Hon.Yusuf Muhammad shugaban karamar hukumar Madagali,yace baya ga abinci suna bukatar tsaro matuka.
Jama’an yankin dai sun nuna jin dadinsu matuka da wannan tallafi da suka samu a yanzu.
Dubban rayuka ne dai suka salwanta,baya ga wadanda aka tilastawa gudun hijira sakamakon rikicin Boko Haram da aka shafe fiye da shekaru shida ana fama,koda yake kawo yanzu hankula sun fara farfadowa a wasu yankunan.
Ga rahoton Ibrahim Abdulaziz da karin bayani.
Facebook Forum