Wata tawagar kwararru daga WHO hukumar lafiya ta duniya ta isa China don shirin fara bincike akan asalin annobar coronavirus.
Cutar da ke haddasa COVID-19, wadda aka yi imanin daga dabbobi ta fara kafin ta fara shafar bil’adama, a wata kasuwar sarin kayayyaki da tuni aka rufe ta a birnin Wuhan da ke tsakiyar China ta fara bulla a cikin shekarar da ta gabata.
Wasu masana daga hukumar WHO da ke Geneva, da suka kware a fannin lafiyar dabbobi da nazarin yaduwar cututtuka a cikin al’umma, zasu gana da takwarorin aikinsu na China a Beijing ranar 11 ga watan Yuli don fidda sharudda da kuma abubuwan da zasu yi bincike akansu, a cewar Tarik Jasarevic, wani mai Magana da yawun hukumar WHO.
“Makasudin nazarin shine zurfafa bincike akan fahimtar dabbobin da cutar COVID-19 ta fara kamawa da kuma yadda dabbobin suka sanya wa mutane cutar, a cewar Jasarevic a wata hira da Muryar Amurka.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 18, 2021
Kungiyar Kasuwanci ta Duniya Na Bukatar Sabon Salon Gudanarwa-Dr. Ngozi
-
Fabrairu 18, 2021
Guterres Ya Yi Kiran a Samar Da Tsarin Bai Daya Na Rigakafin Coronavirus
-
Fabrairu 16, 2021
Kungiyar WTO Ta Gabatar Da Sabuwar Shugaba Ngozi Okonjo-Iweala
-
Fabrairu 16, 2021
Hukumar Lafiya Ta Duniya (WHO) Ta Aminta Da Riga Kafin AstraZeneca
Facebook Forum