Majalisar dattawan Amurka za ta kwashe yinin yau Alhamis tana yin tambayoyi ga lauyoyin shugaba Donald Trump da suke kare shi da kuma ‘yan majalisar wakilai da suke gabatar da karar tsige shi.
Zaman na yau na zuwa ne yayin da batun yanke shawara kan barin wasu shaidu su gabata a gaban majalisar ke kara kusantowa.
Sai dai yadda za a kammala wannan zama cikin hanzari, ya dogara ne ga yadda ‘yan Republican da ke da rinjaye a majalisar za su amince da bukatar ‘yan Democrat kan a ji ta bakin wasu jami’an gwamnatin Trump ko akasin haka.
Wannan kuma shi ne batun da ya mamaye zaman da aka yi a jiya Laraba, a lokacin da sanatoci suka mika tambayoyinsu a rubuce.
Amma batun kuma da ya fi daukan hankali shi ne na tsohon mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, John Bolton.
Bolton ya rubuta wani littafi da ba a wallafa ba tukuna, inda ya yi ikrarin cewa, Trump ya fada masa ya rike dala miliyan $391na tallafin soji ga Ukraine.
Ya kuma duaki matakin rike kudaden da nufin har sai shugaban kasar Volodymyr Zelenskiy ya fito fili ya bayyana binciken cin hanci da rashawa kan abokin hamayyarsa wato Joe Biden a cewar Bolton.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 23, 2021
Jirgin Hukumar Sama Jannatin Amurka Ya Isa Tashar Sararin Sama
-
Fabrairu 22, 2021
COVID-19 :Adadin Wadanda Suka Mutu Ya Kusa Rabin Miliyan A Amurka
-
Fabrairu 20, 2021
Amurka Ta sake Komawa Cikin Yarjejeniyar Sauyin Yanayi A Hukumance
-
Fabrairu 17, 2021
Texas-Dussar Kankara Ta Haifar Da Dauke Wuta A Gabashin Amurka
Facebook Forum