A yau Alhamis Majalisar Dattawan Amurka ta fara sharar fage kan shari’ar tsige shugaba Donald Trump, tare da zaman farko, da zai hada da ‘yan majalisar wakilai.
'Yan majalisar wakilan, su za su zama masu gabatar da kara kan kudurin tsige shugaba Trump a majalisar dattawan, wacce za ta yanke hukunci a karshe.
Za a rantsar da Alkalin alkalan katun kolin Amurka, Justice John Roberts, a matsayin wanda zai sa ido kan shari’ar, kana daga bisani ya rantsar da sanatoci 100 na majalisar dattawan.
Dan majalisar wakilai a bangaren ‘yan Democrat, Jerrold Nadler, na daya daga cikin mutum bakwai da za su gabatar da da karar tsige Trump a gaban majalisar Dattawan.
Ya ce, “mun samu sabbin bayanai da shaidu, wadanda suka nuna cewa shugaban ya yi laifi, sannan mun gano wani yunkuri, da wasu a majalisar Dattawan ke yi, na yin shari’a mara sahihanci.”
Shugaban masu rinjaye, Mitch McConnel ya ce matakin karshe na yau Alhamis, zai sanar da fadar White House da “kirawo shugaban kasa don ya amsa tuhume-tuhumen tsige shi da kuma turo lauyansa.
Za dai a fara ainihin shari’ar ne a ranar Talata mai zuwa.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 23, 2021
Jirgin Hukumar Sama Jannatin Amurka Ya Isa Tashar Sararin Sama
-
Fabrairu 22, 2021
COVID-19 :Adadin Wadanda Suka Mutu Ya Kusa Rabin Miliyan A Amurka
-
Fabrairu 20, 2021
Amurka Ta sake Komawa Cikin Yarjejeniyar Sauyin Yanayi A Hukumance
-
Fabrairu 17, 2021
Texas-Dussar Kankara Ta Haifar Da Dauke Wuta A Gabashin Amurka
Facebook Forum