Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Majalisar Dinkin Duniya Ta Bukaci A Gudanar Da Zabe a Damokaradiyar Congo


Zanga zangar kira ga Shugaba Joseph Kabila ya sauka daga karagar mulki
Zanga zangar kira ga Shugaba Joseph Kabila ya sauka daga karagar mulki

Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya yayi kira ga hukumomi a jamhuriyar Demokaradiyar Congo cewa kada su kara jinkirta babban zaben kasar , suyi kokari suyi zaben kamar yanda aka tsara yi a karshen wannan shekara.

A cikin wannan dambarwar siyasa a kasar, akwai yiwuwar fadawa cikin wani rudami da zai sa a sake dage zaben, a cewar Antonio Guterres, a cikin rahoton da ya aikewa kwamitin sulhun a kan ayyukkan hukumar kwantar da tarzoma ta Majalisar Dinkin Duniya a Congo da ake kiranta MONUSCO.

Gwamnatin da yan adawa sun kulla wata yarjejeniya a ranar 31 ga watan Disamban 2016, wanda ke kira ga shugaba Joseph Kabila ya sauka daga mulki bayan zabe a 2017. Amma sai aka yi ta jinkirta wannan zaben, lamarin da ya janyo yakin basasa a kasar, kuma ya haifar da fargaban cewa Kabila mai shekaru 46 a duniya zai nemi karin wa’adin mulki don ya dora a kan shekaru 17 da ya kwashe yana mulkin kasar.

Yanzu dai zabukkan da zasu hada da na yan majalisar dokoki da na kananan hukumomi, an shirya za’a yi su ne a ranar 23 ga watan Disamban wannan shekarar 2018.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG