Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Majalisar Dinkin Duniya Ta Tabbatar Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Yamal


Kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya a kan batun Yamal
Kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya a kan batun Yamal

Kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya(MDD) bai daya ya tabbatar da yarjejeniyar tsagaita wuta a yankin birni Hodeida mai tsahar jirgin ruwa kuma birnin mai muhimmanci a Yamal.

An cimma wannan yarjejeniya ce a wata tattunawa tsakanin bangarori masu gaba da juna a Yamal da MDD ta jagoranci a makon da ya gabata a babban birnin kasar Sweden.

Kudurin ya amince da duk wata yarjejeniyar da bangarorin suka cimma a birnin Stockholm, inji jakadiyar Birtaniya a kan kwamitin Karen Pierce da tawagarta da shirya daftarin. Muhimman abubuwa dake kunshe a cikin yarjejeniyar sun hada da tsagaita wuta, da kuma janye sojoji a birnin Hodeida kuma hakan ya fara daga ranar 18 ga watan Disemba. Kudurin ya kuma umarci MDD ta taimaka wurin aiwatar da yarjejeniyar da kuma sa ido a kan batun.

MDD zata sa ido a kan tsagaita wuta kuma kamar yanda kudurin ya bata umarni, zata fara tura tawagarta ta farko a kan wannan batu da zasu kwashe tsawon kwanaki talatin a wurin, karkashin jagorancin tsohon kwandan rundunar kwantar da tarzoma ta MDD kuma dan kasar Netherlands General Patrick Cammaert kuma tuni an riga an tura shi yankin.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG