Wannan jan ‘kafa da yan majalisar ke yi akan aiwatar da kasafin kudin, yasa akasarin yan Najeriya tunanin ko siyasa ta shiga cikin al’amarin, musammam a wannan lokaci da shugaban majalisar dattawa Abubakar Bukola Saraki, yake fuskantar tuhuma a kotin kula da da’ar ma’aikata.
Wasu dai na ganin jinkirin ya kara ta’azzara damuwa ta rashin isasshan abinci da tsadar kayan masarufi a kasuwannin kasar.
Sanata Yusuf Abubakar Yusuf ya bayyana hujjar rashin aiwatar da kasafin, inda ya bayyana yadda tsarin da kasafin kudin yakamata ya bi daki daki, kasafin dai zai fara zuwa gurin kwamiti su fara duba shi, sannan a turashi majalisar wakilai bayan nan ya kara dawowa majalisar dokoki, wanda yanzu haka ba a kare aikin sa ba wanda ake sa ran zuwa mako mai zuwa idan Allah ya kaimu za a gabatar da kasafin.
Shi kuma Hon. Garba Garba Chedi, yace akwai wasu yan shirye shirye kalilan wanda ba a karasa ba. ya kuma ce in sha Allahu ranar Talata mai zuwa kasafin kudin zai wuce majalisa.
Kasafin kudin na bana wanda shine kasafin farko na gwamnatin Mohammadu Buhari, wanda ke zaman zakaran gwajin dafi a alamin cika alkawarin da yayi na kawo canji da walwala a kasa.
Domin karin bayani.